BISHARAR DA MANYAN ANNABAWA SUKAYI NA SAMUN CIKIN ANNABI MUHAMMADU S.A.W.
!
!
!
Watan Farko Wato Watan Rajab, Annabin da Ya Fara Zuwa Wajen Sayyida Amina A.S. Ya Gaida Annabi Kuma Yayi Mata Bishara Shine: ANNABI ADAMU A.S. Yazo Yana Haske Ya Kamshi Ya Duka a gabanta Yana cewa: “Barka Da zuwa Ya Shugabanmu Annabi Muhammadu S.A.W. Nazo ne In Gaisheka Kuma In Sallama maka Ya Rasullah”.
!
!
Sayyida Amina A.S. Tace Ban ganeka ba, Wanene kai? Sai Yace: Ai nine “Annabi Adamu Abul Bashar nazo ne inyi masa Muba’ya’a” Kuma Ina Yi miki Bishara cewa :”Kin Sami Cikin Shugaban Halittu Gaba Daya”.
!
!
Sayyida Amina Tace Annabi S.A.W. Yana Ciki amma Ya amsawa Annabi Adamu A.S. Sallama Kuma Ya Sanya Masa Albarka.
!
!
Kaji Wanda Annabawa ma suke Neman Albarkansa ANNABI MUHAMMADU S.A.W.
!
!
A WATA NA BIYU Watan Sha’aban ANNABI SHISU A.S. Sai Ga Wani Annabin Yana Haske Yana Kamshi Shima Ya duqa Gaba Sayyida Amina yace: “ASSALAMU ALAIKA YA RASULALLAH”.
!
!
Sayyida Amina A.S. Tace: “Ban Ganeka Ba” Sai Yace: "Ai nine Annabi Shisu A.S. Nazo ne inyi Muba’ya’a agareshi Kuma Inyi miki Bishara “Kin sami Cikin Mai Tawili Da Hadisi”.
!
!
Shima Yaji Muryar Annabi S.A.W. Ya Sanya Masa Albarka. Allah Kasa Annabi S.A.W. Yasanya Mana Albarka Da Wannan Maulidi Da Mukeyi.
!
!
WATA NA UKU Watan Ramadan Zuwan ANNABI IDRISU A.S.
!
!
Yazo Yana Haske Yana Kamshi Ya Duqa Gaban SayyidaAmina Yace:
“ASSALAMU ALAIKA YA NABIYULLAH”. Sayyida Amina A.S. Ta Tambayeshi Wanene Kai?. Sai Yace: "Nine Annabin Allah Annabi Idrisu nazo inyi miki Bishara Da Samun Wannan Ciki Mai Albarka Kuma Nazo ne In Sallama masa.
!
!
Kuma Ina yi miki bishara Kin Sami Cikin “LU’U LU’U MAI TSADA”.
!
!
“Ina Maki Bishara Domin Kin Sami Cikin”.
!
!
Annabi S.A.W. Ya Amsa Kuma Yasa Masa Albarka.
!
!
Allah Kayi mana Albarka Albarkacin Albarka shine Annabi Muhammadu S.A.W.
!
!
WATA NA HUDU Watan Shawwal ANNABI NUHU A.S. Ya sami Sayyida Amina A.S.Yana Kamshi Yana Haske Ya duqa yace: “ASSALAMU ALAIKA YA HABIBULLAH”.
!
!
Nazo ne In sallama maka Ya Rasullah, Kuma Ina Yi miki Bishara da cewa: “Kin sami Cikin Ma’abocin Nasara Da Fatahohi”.
!
!
Annabi S.A.W. Ya Amsa Kuma Ya Sanya Masa Albarka.
!
!
WATA NA BIYAR Watan Zul~Qada ANNABI HUDU A.S. Yana Haske Ya duqa a gaban Sayyida Amina A.S. Yace: “ASSALAMU ALAIKA YA SAFWATULLAH”.
!
!
Nazo ne nayi Muba’ya’a Kuma Inyi Miki Bishara cewa: “Lallai Kin sami Cikin Fiyayyen Duk Abin Haihuwa”.
!
!
Wadannan fa dukansu Annabawa ne
Kaji Yadda Suke Neman Fada wajen Annabi Muhammadu S.A.W. To Yaya Kai? Yaya Ni? Yaya Ke?.
!
!
WATA NA SHIDA WATAN ZUL~HAJJ Zuwan Annabi IBRAHIM A.S. Yazo Yana Haske Yana Kamsi Ya Duqa A Gaban Sayyida Amina A.S. Yace: “ASSALAMU ALAIKA RAHMATALLAH”.
!
!
Ya Gaishe Da Annabi S.A.W. Yayi Ma Sayida Amina A.S. Bishara da cewa: “Haqiqa Kin Sami Cikin Annabi Mai Girma”.
!
!
Annabi Ya Amsa masa ya sanya masa Albarka.
!
!
WATA NA BAKWAI Watan Al~Muharram Zuwan Annabi Isma'il A.S. Shima Yazo da kakkyawan Fuska Yana Haske Ya Gaida Annabi S.A.W. Yace: “ASSALAMU ALAIKA YA MANIKHTARAHULLAH”.
!
!
Yace Nine Annabi Isma’il A.S. Nazo in gaida shugaba kuma Inyi miki Bishara cewa: “Kin Sami cikin Ma’abocin Falala Ingantacce”.
!
!
Annabi S.A.W. Ya Amsa Kuma Ya Sanya Masa Albarka.
!
!
WATA NA TAKWAS Watan Safar ANNABI MUSA A.S.
!
!
Yayi Sallama Yana Gaida Annabi Yana cewa: "ASSALAMU ALAIKA YA HIRATULLAH". Yace mata Nine Annabin Allah Annabi Musa A.S. Nazo ne Domin In Miki Bishara cewa: “Hakika Kin Sami Cikin Wanda Allah Zai Bashi Alqur’ani Mai Girma".
!
!
"LA'ILAHA ILLALLAH" SAURA WATA DAYA ANNABI S.A.W. YA ZO DUNIYA A SHARI'A KENAN.
!
!
WATA NA TARA WATAN RABI’UL AWWAL Zuwan ANNABI ISAH A.S. {Rahillahi}. Ku sani Fa A Wannan Wata ne Daren Sha Biyu Ga Wata Daren Litini Annabi Muhammadu S.A.W. Ya Sauka A Duniya.
!
!
Sayyida Amina A.S. Taga Wannan Bako Yazo Yana Haske Yana Qamshi. Ya duqa yace: “ASSALAMU ALAIKA YA RASULALLAH”.
!
!
Yace mata Nazo ne inyi maki Bishara domin kin sami cikin “Annabin Allah abin karramawa abin Girmamawa”.
!
!
Annabi Muhammadu S.A.W. Yasanya Masa Albarka Tun Yana Ciki.
!
!
Kaji Dai Yadda Ake Neman Fada A Wajen Annabi Muhammadu S.A.W.
!
!
Don Allah Idan Ka Karanta Wannan Kayi Salatil Fatihi Kafa Daya Ga Annabi S.A.W.
!
!
ALLAHUMMA SALLI ALA SAYYIDINA MUHAMMADIN WA ALA ALIHI HAQQA QADRIHI WA MIQDARIHIL AZEEM.